Shahararren mawakin Najeriya kuma marubucin wakoki Burna Boy zai kasance mawakin da zai cashe a lokacin fafata wasan karshe na gasar cin kofin zakarun Turai da za a yi a Istanbul.
Hukumar UEFA ta sanar da cewa: "Mawakin da ya lashe kyautar lambar yabo ta Grammy, marubucin wakoki kuma furodusa Burna Boy zai kasance mawakin da zai nishadantar a wasan karshe na gasar zakarun Turai na 2023 a filin wasa na Atatürk na Istanbul ranar 10 ga Yuni."
Daga: [Fagen Wasanni]